Hukumar zaben ta kasa INEC ta bude damar yin zabukan fitar da gwani ga jam'iyyu

 Jadawalin zaɓen 2027 ya fara daga yau inda hukumar zabe ta kasa INEC ta bude wa’adin kwanaki 38 ga jam’iyyun siyasa domin gudanar da zaben fitar da gwani.


Daga yau 23 ga Afrilu zuwa 30 ga Mayu, 2026, jam’iyyun siyasa za su gudanar da fitar da gwani na mukaman shugaban kasa, gwamna, yan majalisar dokoki ta kasa da na jihohi, tare da warware duk wata takaddama da ka iya tasowa.


Haka kuma, an umarci jam’iyyun da su mika rajistar mambobinsu ga INEC akalla kwanaki 21 kafin gudanar da zaɓen fitar da gwani, yayin da ranar 10 ga Mayu, 2026 ta kasance ranar karshe na mika wadannan bayanai.

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

Gwamnan Jihar Yobe, Dr. Mai Mala Buni, Ya Yi Godiya Ga Al’ummar Jihar Yobe, Ya Yi Kira Da A Ci Gaba Da Zaman Lafiya

HAJJI 2026: za a fara jigilar alhazai Najeriya zuwa kasa mai tsarki ranar 3 ga Mayu

Hukumar tsaron kasa (DSS) ta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai